‘Ya’Yan Buhari Guda Biyu Sun Rasu Sakamakon Cutar Sikila

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ‘yayansa biyu ne suka rasu sakamakon cutar Sikila.

 

Buhari ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a wajen wani gagarumin taro da ‘yan uwa da abokan arziki suka shirya masa kan bikin cikarsa shekara 80 da haihuwa a fadarsa.

Talla

 

Yayin da yake jawabi game da rayuwarsa shugaba Buhari ya ce ‘ya’yansa biyu ne – da ya haifa tare da matarsa ta farko mai suna Safinatu – suka rasu sakamakon cutar Sikila.

 

BBC Hausa sun rawaito Buhari ya ƙara da cewa hakan ya tilasta masa yin gwajin ƙwayoyin halitta a lokacin da ya tashi auren matarsa ta yanzu Aisha Buhari.

 

Ya ce ya dage cewa dole sai matar da zai aura ta kasance tana da ƙwayoyin halitta na AA, don kauce wa ɗaukar cutar Sikila ga ‘yayan da zai haifa kasancewar shi yana da ƙwayoyin halitta na AS.

 

Buhari ya auri Safinatu a shekarar 1971. sun kuma haifi ‘ya’ya biyar tare da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...