APC a Adamawa za ta daukaka kara kan hana ta tsayar da dan takarar gwamna

Date:

Daga Aliyu Nasir Zangon Aya

Jam’iyyar APC reshen jihar Adamawa a jiya asabar ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin da kotu ta yanke na dakatar da ita daga tsayar da dan takarar gwamna a zaben 2023 a jihar.

Wata babbar kotun tarayya da ke Yola, a ranar Juma’a da ta gabata, ta soke zaben fidda gwani na jam’iyya mai mulki APC a wannan jihar.
Jam’iyyar ta zabi Aishatu Binani a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar a zaben fidda gwanin da aka soke a ranar 26 ga watan Mayu na wannan shekara. Ta samu kuri’u 430 inda ta doke abokin hamayyarta Nuhu Ribadu wanda ya samu kuri’u 288.
Talla
Alkalin kotun, Abdulaziz Anka, ya kuma ki amincewa da rokon da jam’iyyar ta yi na sake gudanar da sabon zaben fidda gwani, wanda hakan ke nufin jam’iyyar ba za ta samu dan takara a zaben ba.
Nuhu Ribadu dai ya garzaya kotu ne bisa zargin rashin bin ka’ida wajen gudanar da zaben fidda gwani.
Kotun ta ce zaben fidda gwanin bai bi ka’idar zaben 2022 ba, da kundin tsarin mulkin Najeriya, da ka’idojin jam’iyya.
Alkalin ya ce nadin na uwargida Binani ya sabawa sashe na 85 na dokar zabe saboda an yi tazarce a lokacin zaben fidda gwani.
Da yake magana a wani taron manema labarai a  jiya ranar asabar, sakataren jam’iyyar APC na jihar, Raymond Chidama, ya roki magoya bayan jam’iyyar da su kwantar da hankalinsu, ya ce jam’iyyar za ta daukaka kara kan hukuncin.
Ya ce bayan yanke hukuncin ne shugabannin jam’iyyar na jihar suka yi taro inda suka amince su dawo da aikinsu ta hanyar kalubalantar hukuncin a kotun daukaka kara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...