An Rantsar da sabbin Shugabannin kungiyar RATTAWU ta jihar kano

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

An shawarci kungiyar ma’aikatan gidajen rediyo da talbijin da harkokin wasan kwaikwayo ta kasa da su kara jajircewa domin nemawa yan kungiyar hakkokinsu domin ciyar da kungiyar gaba.

 

Shugaban kungiyar kwadago na jihar kano kwamaret kabiru Ado munjibir ne ya ba da wannan shawarar a lokacin gudanar da zaben sabbin shugabanni kungiyar ta Rattawu ta jihar kano, wanda ya gudana a helkwatar kungiyar ma’aikatan lafiya dake unguwa uku yan Awaki a nan kano.

 

Kwamaret minjibir yace kungiyar kwadago ta jihar kano a shirye take domin yin aiki kafada da kafada da Sabon shugabancin kungiyar Rattawu wajen nemawa ma’aikata hakkokinsu, musamman yan fansho da suka kammala aiki ba, a biyasu hakkokinsu ba da kare mutuncin ma’aikata a kodayaushe.

Talla

Shugaban kungiyar Rattawu na kasa kwamaret kabiru bello tsanni, wanda mataimakin kungiyar na Arewa maso yamma kwamaret Abubakar chika ya jagoranta, yace sun fito da Managartan tsare tsare na horas da yan kungiyar da neman hanyoyin gyara musu albashin yan jarida na rediyo da talbijin da kawo sabbin ayyukan da za su inganta ayyukan Yada labarai a koina a fadin kasar nan.

 

Ya shawarci wadannan sabbin shugabanni da su tallafawa kungiyoyinsu ta hanyoyin da suka kamata domin ciyar da kungiyar gaba.

Talla

A jawabinsa Sabon Shugaban kungiyar Rattawu na jihar kano kwamaret Babangida mamuda Bilyaminu ya godewa yan kungiyar bisa zabarsa da suka yi inda ya sha alwashin aiwatar da aiki yadda ya kamata domin ciyar da kungiyar gaba.

 

Hajiya samira Hassan ita ce ta lashe kujarar jami’ar hulda da jama’a ta kungiyar Rattawu reshen jihar kano, wadda ta lashe zabenta babu hamayya a karo na biyu, ta kuma yi alkawarin yin aiki tukuru wajen ganin an ciyar da kungiyar gaba.

Talla

Ta yabawa yan kungiyar ta kasa da ta jiha dangane da goyan baya da suka bata wajen dawowa matsayin ta a karo na biyu, inda ta ba da tabbacin gudanar da aiki cikin gaskiya da rikon Amana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...