Gwamnatin tarayya ta bukaci gaggauta bude kamfanin siminti na Dangote

Date:

Daga Abdulhamid Habib Isa Tukuntawa

Majalisar tsaro ta kasa karkashin jagorancin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ta bada umarnin bude masana’antar siminti na Dangote da ke Obajana a jihar Kogi ba tare da bata lokaci ba.

Majalisar ta bayar da umarnin ne a wani taro da ta gudanar a Abuja, babban birnin kasar.
Talla
Ministan harkokin ‘yan sanda, Mohammed Dingyadi, tare da takwaransa na cikin gida, Rauf Aregbesola da babban hafsan tsaron kasa, Janar Lucky Irabor, sun bayyana wa manema labarai bayan taron cewa fadar shugaban kas ace ta bayar da umarnin nan take.
Talla
Aregbesola ya ce an cimma yarjejeniya tsakanin gwamnatin jihar Kogi da kamfanin Dangote kan bukatar sake bude masana’antar simintin, inda ya bukaci bangarorin biyu su mutunta yarjejeniyar.
Talla
Ministan ya kara da cewa majalisar ta ba da umarnin bude masana’antar nan take tare da ba da shawarar cewa a warware duk wasu batutuwan da ake takaddama a kai a bisa doka domin gwamnati ta himmatu wajen samar da ayyukan yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...