Daga Aisha Aliyu Umar
Sanatan Kano ta kudu Kabiru Ibrahim Gaya ya bayyana Husaini Ambo Indabawa a matsayin Mai magana da yawun sa.
Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya Sanya hannu da kansa Kuma aka aikowa kadaura24.
” Na nada Husaini Ambo Indabawa a matsayin mai magana da yawun na akan duk wasu al’amurana da suka harkokin wakilcin da nake yiwa mutanena na Kano ta kudu da Kuma harkokin Siyasa “. A cewar sanarwar
Sanarwar tace Husaini Ambo ban bashi mukamin ne saboda kwarewar da yake da ita a fannin yada labarai, don haka ana sa ran zai yi duk mai yiwuwa wajen kare mutunci da takarar Sanatan a kafafen yada labarai.
Husaini Ambo Indabawa wanda ake yiwa lakabi da Italy dan jarida ne da ya dade yana aiki da gidan Radio Rahama dake Kano Kuma shi ne wakilin gidan Rediyon a gidan gwamnatin jihar Kano.