Daga Umar Usman Sani Mainagge
Gwamnatin jihar Kano ta titsiye Mutuminan dan Kofar Na’isa da yayi da’awar ya auri aljanna har sun haifi ‘ya’ya da ita.
A gudanar da titsiyen ne a ofishin Kwamishinan ma’aikatar addini ta jihar Kano Dr. Tahar Baba Impossible dake gidan murtala a Nan birnin Kano.
Tun a baya dai Ahmad Ali dake unguwar k/Na’isa Wanda akafi sani da Mai aljana yayi shuhurane da hulda da aljana da bada magungunan gargajiya, harma ya shaidawa kafafan yada labarai dana sada zumunta cewar wai ya auri aljana mai suna ummusibyan harma sun haifi ‘ya’ya tare.
Wancan furuci na Mai aljana ya baiwa Mutane mamaki sosai Saboda yadda yace mahaifin aljanar ne ya aura masa ita Saboda Dama shi a wajen aljanu ya girma sun Saba da juna sosoi.
To Bayan wancan furuci al’umma sun Yi ta kalubalantar Mai aljana ,hakan tasa gwamnatin Jihar Kano magantuwa Saboda yadda al’ummar suka Dauki Maganar da Kuma gujin kada Shi Mai aljanna ya jefa Mutane Cikin bata. Shi ne yasa Gwamnatin ta shirya Wannan Zama a Wannan Rana.
To sai dai a0 Mai aljana yayi karo da goshi jirgi domin yace ya janye duk kalamansa na baya tare da zubda makamansa bayan daya Sha matsa irinta Mai a gaban kwamashinan addinai.
Bayan janye bayanan da yayi a baya Mai aljana ya shaidawa Duniya cewa ya saki Matarsa Amma aljanar har saki uku a gaban al’umma a ofishin kwamashinan Dr. Tahar Baba impossible.
Wakilin Kadaura24 ya tambayi Mai aljana cewa a Bayan mun ji matarka Mutum tace har raba Kwana suke da amaryarka aljana” Mai aljana sai ya kada Baki yace ” kawai dai ta Fadi hakan ne domin ta Kare Mana Abincin mu, Amma Karya take Yi.
A Jawabinsa Kwamishinan harkokin addini na Kano Dr Tahir Baba Impossible yace sun shirya Titsiyen ne domin Gudun kada al’umma su fada Haka ta sanadiyyar kalaman Mai aljanar.