Sama da Mata da Marayu 500 zamu yiwa Kayan Sallah a bana – Abm. Baba Yawale

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa


Wata Kungiyar Tallafawa Mata da Marayu Mai Suna Orphans and Women Support Initiative ta ta dauki Gabarar Taimakawa Talaka da Marayu A Fadin Nigeria, Kuma Tuni Suka Fara da Jihar Kano kasancewar Masu Kungiyar Yan asalin jihar Kano ne.


Cikin Wata sanarwa da Babban Jami’inta dake kula da Arewa Maso yammacin Kasar nan Sadeeq Ali Dakata Aikawa ya Sanyawa hannu Kuma ya aikowa Kadaura24 yace Shugaban Kungiyar ba Kasa Hon. Baba Yawale ne ya bayyana hakan Yayin kaddamar da rabon kayan Sallah a nan Kano.


“Wannan NGO Yana Cigaba Da Rabawa Mabuqata Kayan Sallah Domin Faran Ta Musu Cikin Zuciyarsu Muna Rokon Allah Yasa Alheri Acikin Wan Nan Aiki”. Inji  Ambassador Baba yawale


“Wan Tallafi Irin Aikin Da Allah Yakeso Ne Shiyasa Muke Shiga Kauyukan Da Kammu domin mu raba Kayan domin Neman yardar Allah”. Inji Shi


Amb. Baba Yawale yace Kalla Fiye Da Mutum Dari Biyar (500) Zasu Amfana da  Wannan Tallafin,. Ya kuma ce Kofar su a Bude Take Ga Mai San Saka Hannu Jarin Da Babu Faduwa A Ciki Domin Samun Babban Rabo A Lahira.

 
Sanarwar tace Wanan Aiki da Kungiyar take gudanarwa Babu Ko koban wani Dan Siyasa “Mai Girma DG Wannan Kungiyabda Bata gwamnati ba NGO Shine Yake Daukar Nauyi Tare Damu Masu Taimaka Masa, Muna Da Shirye-Shirye da dama domin tallafawa Al’umma Daban-Daban”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...