Gwamna Sani Bello ya kira taron gaggawa don tattaunawa akan babban taron APC na kasa

Date:

 

Sabon Shugaban Kwamitin Riƙo na APC, Gwamnan Jihar Naija, Abubakar Sani Bello, ya kira taron gaggawa na shugabannin jam’iyar na ƙasa.

A wata sanarwar taron da ya sanya wa hannu da kan sa, tare da kuma Ken Nnamani (Kudu-maso-Gabas), Stella Okotete (Shugabar Mata ta Ƙasa), Sanata Aba Ali (Arewa-maso-Yamma) da kuma Farfesa Tahir Mamman (Arewa-maso-Gabas).

A sanarwar, za a yi taron ne ta yanar gizo a ranar 17 ga watan Maris da misalin ƙarfe 11 na safe.

An yanke hukuncin yin taron gaggawar ne a taron kwamitin riƙo km jam’iyar karo na 26 da ya gudana a ranar Talata.

Sanarwar ta ce an kira taron gaggawar ne ta la’akari da sashe na 25B (i da ii) na kundin tsarin mulkin APC da kuma ikon da a ka baiwa Kwamitin Riƙon a taron da a ka cimma matsaya a kan hakan a ranar 8 ga watan Disamba, 2020.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...