Sabbin Shugabannin Kungiyar yan Tifa na Jihar kaduna sun karbi rantsuwar kama aiki

Date:

Daga Sani Abdulrazak Darma

An bukaci sabbin Shugabannin Kungiyar ‘yan Tifa na Jihar Kaduna da su zamo masu gaskiya da Adalci da kuma aiki tukuru.

Bayanin Hakan ya Fito ne ta bakin guda daga cikin Iyayen Kungiyar na kasa Reshen Arewa Alh Husaini Adamu, yayin Rantsar da Sababbbin Shuwagabannin Kungiyar ‘yan Tifa ta Kasa reshen Jihar Kaduna.

Alh Husaini Adamu yace sana’ar Tifa a bace wacce take da albarka da kuma taimakawa wajen samar da aikin yi ga matasa tare Kuma da bunkasa tattalin Arzikin kasa.

Adamu ya bukaci Sababbbin Shuwagabannin Kungiyar ta ‘yan Tifa na Kaduna da su rinka yiwa ‘ya’yan Kungiyar bita akai-akai domin kaucewa fadawa cikin wata matsala.

Alh Husaini Adamu ya godewa gwamnatin Jihar Kaduna data Sanar da fili kyauta ga Kungiyar Direbobin Tifar, da kuma basu damar yin amfani da Filin bisa ka’ida.

Tun da fari a nasa jawabin Sakataren Kungiyar ‘yan Tifa na Jihar Kano Wanda ya wakilcin Shugaban Kungiyar Commared Mamuni Ibrahim Takai, ya ja hankalin Direbobin dasu zamo masu biyayya, da kuma yin tuki batare da ganganci ba.

Yayin da yake Jawabin sa bayan ya karbi Rantsuwa Sabon Shugaban Kungiyar  Commared Muhd Sani Ja’afar ya bayyana farin cikin sa, inda ya yi kira ga duk masu tuka motar Yashi, Kasa, Dutse dasu bashi hadin kai domin ciyar da Kungiyar gaba.

Sani Ja’afar yace zai iya bakin kokarinsa domin Samar da cigaba a Kungiyar tare da yin Adalci ga kowa.

Wakilin Kadaura24 daga can Jihar ta kaduna ya rawaito mana cewar tarony ya samu halartar Jami’an dake kula da hanya na Kaduna, da kuma Jami’an tsaro daga kowane bangare domin tabbatuwar lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...