Rasha ta ce ta kwace babbar tashar nukiliya ta kasar Ukraine

Date:

Gwamnatin Rasha ta gaya wa hukumar da ke sa ido kan harkokin nukiliya ta duniya cewa, a yanzu haka yankin da babbar tashar nukiliya ta Ukraine take, kusa da birnin Zaporizhzhia na kudanci yana karkashin ikonta.

Hukumar nukiliyar, IAEA, ta ce Rashawan sun ba ta tabbacin cewa ma’aikatan Ukraine da ke aiki a tashar na ci gaba da gudanar da ayyukansu.

Sai dai hukumar nukiliyar Ukraine ta ce tana tattaunawa da dukkanin tashoshinta na nukiliyar, kuma aiki na ci gaba da gudana a dukkanninsu.

Amma Darakta Janar na hukumar nukiliyar ta duniya, Rafael Grossi, ya shaida wa taron manema labarai cewa halin da ake ciki na da tayar da hankali

Ya ce abu mafi muhimmanci a nan shi ne, idan ana rikici, lalle akwai fargabarkai hari, ko kuma ma a samu hadarin tashin makaman.

Tashar Zaporizhzhia tana dauke da shida daga cikin na’urorin nukiliya 15 na Ukraine.

BBC Hausa ta rawaito kafin yanzu dai hukumomin da ke kula da nukiliyar Ukraine sun bukaci taimakon hukumar nukiliya ta duniya, da ta taimaka ta tabbatar da tsaro a cibiyarta ta Chernobyl da ke arewacin Ukraine, wadda dakarun Rasha suka kwace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...