Hotuna na da Aisha Humaira ba na aure ba ne, na talla ne – Inji Mai-shadda

Date:

Fitaccen Mai tsara fina-finan Hausa na Kannywood, Abba Bashir, wanda a ka fi sani da Mai-shadda ya musanta rahotannin da ke yawo a kafafen sadarwa cewa zai auri jaruma Aisha Ahmad, wacce a ka fi sani da Aisha Humaira.
A yau Alhamis ne dai Kadaura24 ta rawaito cewa Mai-shadda na daf da angwance wa da Aisha Humaira, bayan da ya wallafa hotunan da su ka ɗauka tare a shafinsa na Instagram.
“Zan yi wuff da gishiri ambassador.”, haka Mai-shadda ya rubuta a saman hotunan da ya wallafa a Instagram ɗin.
Bayan wallafar da ya yi, jaruma Aishat Humaira ta sake wallafa hotunan a shafinta na Instagram, inda ta haɗa da alamar soyaiya.
Hakan ne ya sanya a ka dinga yayata wa cewa aure jaruman na Kannywood za su yi.
Sai dai kuma wata majiya da ke kusa da Mai-shadda, a yammacin Alhamis ta shaida wa Daily Nigerian Hausa cewa hotunan ba na aure ba ne, na talla ne.
A cewar majiyar, jaruman biyu sun ɗauki hotunan ne domin yi wa Kamfanin Shehu Danƙwarai da ke kasuwar Kantin Kwari.
Majiyar ta ce nan ba da daɗewa ba Mai-shadda zai wallafa tallan a shafinsa na Instagram.
“in an jima kaɗan ma zai saki tallan a kan Instagram ɗin shi sabo da mutane su na ta damun shi da waya.
“Tallan Kamfanin Shehu Danƙwarai ne, in an jima zai sanya shi a Instagram,” in ji majiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Karyata Rahoton Cibiyar Wale Soyinka Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton da...

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Cire Maryam Sanda Daga Jerin Wadanda Za a Yi Wa Afuwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bada umarnin a...

Majalisar Kano ta buƙaci a soke ɗaukar aikin kwastam da aka yi a kwanan nan

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga dukkan...

‎ ‎Kuskure ne Tinubu ya cigaba da ciyo wa Nigeria bashi bayan ya cire tallafin mai – Sarki Sanusi

‎ ‎ ‎Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN),...