NUT ta yabawa Ganduje bisa nadin sabon jami’in kula da Tsangaya a Jihar Kano

Date:

Halima M Abubakar
Kungiyar malamai ta Najeriya reshen karamar hukumar Gwale ta bayyana nadin Malam Mustapha Adamu sabon jami’in  kula da Tsangaya na Jihar kano a matsayin wanda ya dace.
 A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren kungiyar reshen karamar hukumar Kwamared Auwalu Shuaibu Ja’e kuma aka aikowa Kadaura24.
Sanarwar ta kuma bayyana Malam Mustapha Adamu a matsayin jami’i mai kwazo da sadaukar da kai wajen bunkasa ilimi a kananan hukumomi da jiha baki daya.  .
Sanarwar ta ce kungiyar ta yabawa gwamnatin jihar bisa wannan nadin da kuma kokarin da take yi na inganta fannin ilimi a jihar kano.
 Malam Mustapha Adamu har zuwa lokacin da aka nada shi, shi ne Shugaban sashin Larabci a Hukumar Ilimi ta Karamar Hukumar Gwale.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rashin tsaro: Tinubu na ganawar sirri da shugabannin hukumomin tsaro na ƙasa

A halin yanzu shugaba Bola Ahmed Tinubu ya na...

Ban ce filin makarantar Bechi nawa ba ne, Kuma zan taimaka wajen gini Makarantar – Alh. Sagir Jaen

Daga Maryam Muhammad Ibrahim Biyo bayan koken da al'ummar garin...

Ƴan majalisar wakilai 2 na NNPP a Kano sun fice daga jam’iyyar zuwa APC

Wasu ‘yan majalisar wakilai biyu daga jihar Kano sun...