Bazan dawo Nigeria ba sai an bani tabbacin Kare lafiya ta – Jaafar Jafaar

Date:

Ɗan jaridan da ya fitar da jerin bidiyon da ke zargin Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da karɓar cin hanci ya ce ya bar Nijeriya ne saboda ba shi da ƙwarin gwiwar hukumomi za su kare rayuwarsa.

Cikin hirarasa da BBC Hausa daga Ingila, Ja’afar Ja’afar ya ce zai ci gaba da neman mafaka a Birtaniya tare da iyalinsa har sai ya samu tabbacin za a kare rauywarsa idan ya koma Najeriya.

Kazalika, ya yi zargin cewa cin hanci da rashawa a gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari sun ƙara ta’azzara, inda ake yaƙar masu fallasa badaƙalar maimakon ainihin masu aikata cin hancin.

A shekrar 2018 ne mawallafin jaridar Daily Nigerian ɗin ya saki wasu bidiyo da ke zargin cewa Gwamna Ganduje ne yake karɓar damman daloli daga hannun wani ɗan kwangila a matsayin cin hanci.

Sai dai gwamnan ya sha musanta zargin yana mai cewa ƙirƙirar bidiyon aka yi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...