Gwamnan Taraba ya bayyana dalilinsa na shirin komawa APC

Date:

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai shiga jam’iyyar APC a ranar 19 ga Nuwamba.

A wata tattaunawa da ‘yan jarida a ranar Asabar, gwamnan ya bayyana a hukumance cewa zai bar jam’iyyar PDP zuwa jam’iyya mai mulki.

Kefas ya ce sauyawar jam’iyyar “na da nasaba da makomar mutanen Taraba.

InShot 20250309 102512486

“Za a sami babban sauyi da daidaituwa a ranar 19 ga Nuwamba,” in ji gwamnan.

“Zan sauya sheka a hukumance daga PDP zuwa APC. Wannan sauyi yana da alaka kai tsaye da makomar al’ummar Taraba.”

Kefas shi ne sabon gwamna na baya-bayannan da ya bar PDP zuwa APC a shekarar 2025.

Sauran gwamnonin da suka sauya sheka daga PDP zuwa APC sun hada da Umo Eno na Akwa Ibom, Sheriff Oborevwori na Delta, Peter Mbah na Enugu, da Douye Diri na Bayelsa.

A 2023, Kefas ya lashe zaben gwamnan Taraba da kuri’u 257,926.

Ya doke Muhammad Yahaya na jam’iyyar NNPP da Emmanuel Bwacha na APC.

Tun daga 1999, duk gwamnonin Taraba sun kasance ‘yan jam’iyyar PDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ɗaliban Mariri ta gudanar da aikin duba marasa Lafiya kyauta a yankin

Daga Abdallahi Shu'aibu Hayewa   Kungiyar Dalibai ta Makarantar Mariri wato...

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...