Yadda ƴansanda suka kama wasu da suke zargin ƴanbindiga ne a Kano

Date:

Rundunar yansanda ta Kasa reshen jihar Kano ta ce ta yi nasarar kama wasu da take zargin yanbindiga ne masu satar mutane domin kudin fansa.

Rundunar yansandan ta ce ta kama mutum biyu a ranar Asabar a yankin Shanono bayan samun bayanan sirri.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa Jami’in hulda da jama’a na rundunar yansandan jihar Kano ya shaida wa BBC cewa yanbindigar sun shigo ne daga jihar Katsina da ke makwabtaka da Kano.

Wannan na zuwa bayan mazauna yankin ƙaramar hukumar Shanono a jihar Kano sun koka game da yadda ‘yanbindiga masu satar mutane suka fara addabarsu suna satar mutane da kuma dabbobi.

SP Kiyawa ya tabbatar da cewa an samu kutsen wasu da ake zargin ƴanbindiga ne a yankin ƙaramar hukumar Shanono kuma suna satar mutane da dabbobinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tsofaffin Kansiloli Sun Yi Saukar Alƙur’ani da Addu’a na Musamman ga Gwamna Abba

  Ƙungiyar tsofaffin kansiloli na jihar Kano ta gudanar da...

Hisbah ta kama mutane 25 bisa zargin shirya auren jinsi a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama akalla mutane...

Rikici a Bebeji: Jigon Kwankwasiyya na zargin an shirya cire sunayen tsoffin kansiloli domin yin kashe-muraba

Wani jigo a tafiyar Kwankwasiyya a karamar hukumar Bebeji...

KANFEST 2025: Gwamna Abba ya umarci sarakunan Kano da su ci gaba da hawan sallah

  Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya umarci...