Muna rokon gwamnatin Kano ta haramta daukar fasinjoji a bakin titi – Kungiyar Direbobin Haya

Date:

Ƙungiyar Direbobin Motocin Haya ta ƙasa reshen Kano dake tashar Kofar Wambai ta roƙi Gwamnatin Jihar Kano da ta kafa kwamitin kar-ta-kwana domin sa ido kan tashoshin mota da ke ɗaukar fasinjoji ba bisa ƙa’ida ba.

Shugaban ƙungiyar tashar motoci ta Kofar Wambai, Alhaji Salisu Sani Yau Gareka, ne ya yi wannan kira a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishin ƙungiyar dake cikin tashar.

Alhaji Salisu ya ce ɗaukar fasinjoji a bakin titi na kawo cikas ga ci gaban harkar sufuri a jihar Kano, lamarin da ya ce ya daɗe yana damun masu sana’ar.

“Akwai buƙatar Gwamnati ta ɗauki matakan da za su kawo ƙarshen wannan matsala wadda ta jima tana hana harkar sufuri ta bunƙasa kamar yadda ya kamata, kamar yadda ake gani a wasu jihohi.” a cewasa

Rijistar Zabe: Gidan Rediyon Kano Ya Ƙara Zage Dantse Wajen Wayar da Kai Kan Al’umma

Ya ƙara da cewa ƙungiyar tashar Kofar Wambai za ta ci gaba da mara wa Gwamnatin Jihar Kano baya a duk wani shiri da zai kawo cigaban harkokin sufuri.

Shugaban ƙungiyar ya yi nuni da cewa kamar yadda Kano ta yi suna a harkar kasuwanci, za ta iya samun gagarumar nasara a fannin sufuri idan aka samu tsari na gaskiya da bin dokoki.

FB IMG 1753738820016
Talla

Haka kuma, ya shawarci direbobin haya a jihar Kano da su riƙa bin ƙa’idar shiga tashoshin mota don kaucewa asarar kudaden shiga na gwamnati, domin waɗannan kuɗaɗen su ne ke taimaka mata wajen gudanar da ayyukan raya jiha.

Daga ƙarshe, Alhaji Salisu ya tabbatar da cewa ƙungiyar tashar Kofar Wambai za ta ci gaba da goyon bayan manufofin gwamnati, musamman wajen samar wa matasa ayyukan yi don rage shaye-shaye, sata da sauran munanan dabi’u. Ya kuma yi kira ga mambobin ƙungiyar da su ƙara ɗaurewa wajen mara wa ƙungiyar baya domin ci gaban al’umma baki ɗaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hasashe 6 da Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi kuma suka tabbata a siyasar Kano

‎ ‎ ‎ ‎Musa Iliyasu Kwankwaso na daga cikin fitattun ’yan siyasar...

Hukumar Hisbah Za ta Tura Sama da Jami’ai 1,000 Don Samar da Tsaro a Ranar Takutaha a Kano

Hukumar Hisbah ta Karamar Hukumar Birni a Jihar Kano...

Kotun tafi-da-gidanka ta KAROTA ta ayyana neman wani direba ruwa a jallo

Alkalin Kotun Majistare da ke gudanar da shari’ar masu...

Rijistar Zabe: Gidan Rediyon Kano Ya Ƙara Zage Dantse Wajen Wayar da Kai Kan Al’umma

Hukumar gudanarwar Gidan Rediyon jihar Kano ta ƙara kaimi...