Da dumi-dumi: Mafarauta sun kama masu garkuwa da mutane a jejin Jihar Kogi

Date:

 

Mafarauta sun samu nasarar cafke wasu da a ke zargin masu garkuwa da mutane ne guda uku a maɓoyar su, kusa da yankin Ossra-Irekpeni a kan hanyar Okene-Lokoja-Abuja.

Ɗaya da ga cikin mafarautan da su ka kai sumamen ya shaidawa jaridar Daily Trust cewa sai da a kai musayen wuta kafin su damƙe mutanen.

Ya ce mafarautan, tare da shugaban Ƙaramar Hukumar Adavi, Joseph Samuel Omuya, su ka kutsa kai cikin dajin bayan samun bayanan sirri.

Daily Nigerian ta rawaito Mafaraucin yana baiyana cewa , bayan sun shiga jejin, sai masu garkuwa da mutanen su ka fara buɗe wuta, sai mafarautan su ka maida martani.

“Nan da nan muna muka buɗe musu wuta har mu ka samu nasarar damƙe uku daga ciki,” in ji shi.

Ya kuma ƙara da cewa wasu daga cikin ƴan ta’addan sun tsere da raunukan bindiga a jikin su.

Bayan Omuya ya yabawa mafarautan a bisa ƙoƙarin da su ka yi na kama ƴan ta’addan, ya kuma yi kira ga mazauna ƙauyuka da su zama su na jajircewa wajen tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar...

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...