Zargin cin zarafi: BBC ta ki karbar takardar ajiye aikin shugaban sashin Hausa

Date:

Gidan Radio BBC, ya dakatar da Editan Sashen Hausa, Aliyu Tanko, na tsawon watanni uku bisa zargin cin zarafi da tsohuwar ma’aikaciyar gidan, Halima Umar Saleh, ta yi masa.

Haka kuma an kafa wani kwamiti na bincike kan ƙorafe-ƙorafe da dama da wasu tsoffin ma’aikata da kuma waɗanda har yanzu ke aiki a BBC Hausa suka shigar kan Tanko.

FB IMG 1753738820016
Talla

An dai naɗa Aliyu Tanko a matsayin editan sashen Hausa a shekarar 2020.

Wata majiya ta shaida wa manema labarai cewa mataimakin shugaban BBC News kuma daraktan BBC News Global, Jonathan Munro, ne ya bayar da umarnin gudanar da binciken, tare da aiko da tawaga daga Landan zuwa Abuja domin gudanar da shi.

Da dumi-dumi: Hadimin Gwamnan Kano ya maka mawallafin Jaridar Daily Nigerian Jafar Jafar a gaban Kotu

Majiyar ta ce an shaida wa Tanko cewa ba zai iya yin murabus ba, yayin da aka dakatar da shi tare da gudanar da bincike .

“An ƙi amincewa da murabus ɗin ne bisa dalilin cewa bai bi ƙa’ida ba. A matsayinsa na babban jami’i, wajibi ne ya bayar da sanarwar watanni biyu kafin a amince da murabus ɗinsa, ko kuma ya biya albashin watanni biyu idan ba ya son jira – haka ma idan kamfanin ne zai kawo ƙarshen aikinsa,” in ji majiyar.

Sai dai a wata tattaunawa da Daily Nigerian, Aliyu Tanko ya tabbatar da cewa ya ajiye aikinsa daga BBC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...