Ganduje ya dawo Nigeria bayan ya shafe wata a Birnin London

Date:

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje, ya dawo Najeriya daga Landan a jiya Laraba.

Tsohon gwamnan jihar Kanon ya tafi ƙasar Birtaniya domin neman magani jim kaɗan bayan murabus ɗinsa daga shuagabancin jam’iyya mai mulki a ƙasar.

FB IMG 1753738820016
Talla

Da ya ke tabbatar da wannan batu ga jaridar The PUNCH, tsohon shugaban ma’aikatansa, Mohammed Garba, ya ce Ganduje ya sauka a Nijeriya ne a safiyar jiya Laraba bayan shafe kusan wata guda a waje.

Gwamna Abba ya rantsar da sabon shugaban hukumar hana cin hanci da rashawa ta Kano

“Eh, ya dawo Najeriya yau. Ya dawo cikin koshin lafiya, kuma ya ƙarasa gidansa,” in ji Garba, yayin da ya ke tabbatar wa da jaridar PUNCH.

Ya ƙara da cewa Ganduje ya bar Najeriya zuwa Landan ne kwana biyar bayan ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar domin neman lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...