Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Date:

Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe ta dakatar tare da soke zaɓen cike gurbi da ke gudana yanzu haka a jihar Kano saboda “tashin hankali”.

FB IMG 1753738820016
Talla

Wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar ta ce ‘”‘yandaba sun tarwatsa kayayyakin zaɓe a ƙananan hukumomin Bagwai da Shanono da Gari”, inda ake gudanar da zaɓen ɗanmajalisar tarayya.

A cewarta: “Cigaba da kaɗa ƙuri’a a irin wannan yanayin na dabanci da tilasta wa masu zaɓe ya saɓa da tanadin dimokuraɗiyya na gudanar da sahihin zaɓe, kuma zai koyar da satar ƙuri’a da ba za a yarda da shi ba,” in ji sanarwar.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Duk da cewa APC ce riƙe da mulkin a tarayya, NNPP ce mai mulki a jihar ta Kano da ke arewacin ƙasar.

Zuwa yanzu ba a kai ga samun sakamakon zaɓen a hukumance ba, yayin da ake ci gaba da kaɗa ƙuri’a a wasu rumfunan zaɓen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...

A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

Hukumar zabe mai zamanta ta Kasa ta bayyana Dan...

PDP ta yi watsi da zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono dake Kano

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya...

Zabe:An kama ƴandaba sama da 100 da ake zargi da yunkurin tada tarzoma a Kano – INEC

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta...