Rikicin APC : Ranar Litinin Za’a Fara Sulhunta Bangaren Ganduje da Shekarau

Date:

Daga Nura Garba Jibril
Kwamitin sulhun jam’iyyar APC ya baiwa ‘yan Najeriya tabbacin yin adalci ga fusatattun ‘yan jam’iyyar da Suka gabatar da korafin su ga Uwar jam’iyyar domin samun zaman lafiya mai dorewa a Jam’iyyar.
 Shugaban kwamitin Sanata Abdullahi Adamu kuma tsohon gwamnan jihar Nasarawa ne ya bada wannan tabbacin a wata ‘yar gajeriyar hira da manema labarai a Abuja.
 Sanata Abdullahi ya ce manufar ita ce a tabbatar da an sulhunta duk wadanda suka samu sabani  kafin babban taron jam’iyyar na kasa ya zo nan ba da dadewa ba.
 Shugaban Kwamitin ya kara da cewa, shugabannin jam’iyyar sun damu matuka da Matsalolin da Suka dabai baye Jam’iyyar Musamman a matakan jihohi, Inda ya bada tabbacin zasu Samar da zaman lafiya tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar ta kowane hali.
 Sanata Abdullahi Adamu ya ce kwamitin ya yanke shawarar fara aikinsa a jihar Kano a Ranar litinin din nan domin warwaren Matsalar da jam’iyyar APC ta fuskanta don ya Zama masomin Nasarar Kwamitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...