Rikicin APC : Ranar Litinin Za’a Fara Sulhunta Bangaren Ganduje da Shekarau

Date:

Daga Nura Garba Jibril
Kwamitin sulhun jam’iyyar APC ya baiwa ‘yan Najeriya tabbacin yin adalci ga fusatattun ‘yan jam’iyyar da Suka gabatar da korafin su ga Uwar jam’iyyar domin samun zaman lafiya mai dorewa a Jam’iyyar.
 Shugaban kwamitin Sanata Abdullahi Adamu kuma tsohon gwamnan jihar Nasarawa ne ya bada wannan tabbacin a wata ‘yar gajeriyar hira da manema labarai a Abuja.
 Sanata Abdullahi ya ce manufar ita ce a tabbatar da an sulhunta duk wadanda suka samu sabani  kafin babban taron jam’iyyar na kasa ya zo nan ba da dadewa ba.
 Shugaban Kwamitin ya kara da cewa, shugabannin jam’iyyar sun damu matuka da Matsalolin da Suka dabai baye Jam’iyyar Musamman a matakan jihohi, Inda ya bada tabbacin zasu Samar da zaman lafiya tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar ta kowane hali.
 Sanata Abdullahi Adamu ya ce kwamitin ya yanke shawarar fara aikinsa a jihar Kano a Ranar litinin din nan domin warwaren Matsalar da jam’iyyar APC ta fuskanta don ya Zama masomin Nasarar Kwamitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...

Al’ummar Garin Riruwai da wani Kamfanin Hakar ma’adanai Sun Cimma Yarjejeniya Kan Ci gaban yankin

Kwamitin ci gaban Al’ummar garajn Riruwai da wani kamfanin...