Daga Surayya Malam Abba
Shugaban Karamar Hukumar Gabasawa da al’ummar yankin sun yabawa Gwamnatin Jihar Kano bisa Aikin Samar da Rijiyoyin Burtsatse Masu Amfani da hasken rana Guda buyu da aka gudanar a yankinsu.
Kadaura24 ta rawaito Shugaban Karamar Hukumar Alhaji Mahe Garba Garun Danga ya baiyana hakan ne Lokacin kaddamar da Sabbin Rijiyoyin Burtsatse Guda 2 da aka gudanar a Karamar Hukumar sa bisa sahallewar Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar Kano.
Shugaban Karamar Hukumar yace ya Zama wajibi su yabawa Gwamnatin Saboda Aikin Zai fitar da dumbin al’umma daga Matsalar Ruwan Sha da Kuma inganta Lafiyar su.
Yace an gudanarwa da aikin Rijiyoyin Burtsatse ne a Garuruwan Garun Danga da Kwazari duk a Karamar Hukumar ta Gabasawa.
Alhaji Mahe Garba yace an Kashe Sama da Naira Miliyan 21 waje Gina Rijiyoyin Burtsatse Masu Amfani da hasken rana, Wanda ya baiya hakan a Matsayin Wani yunkuri da Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Kwamishina Kananan Hukumomi Alhaji Murtala sule Garo ke yi don fitar da al’umma daga dukkanin Wata Matsala.
Ya bukaci al’ummar garurun da aka gudanar da Aikin da su baiwa Aikin kulawar data dace domin su Dade Suna Amfana da Aikin,tare Kuma da yi musu alkawarin sake kai musu Wasu aiyukan da zasu inganta Rayuwar su.
A nasu jawabin, Manyan limaman garurun Garun Danga da Kwazari Malam Waliyillah Muhd da Malam Abdullahi Musa sun godewa Kwamishina Murtala sule Garo da Shugaban Karamar Hukumar bisa Aikin Rijiyoyin Burtsatse da aka yi musu Wanda suka ce sun dade Suna bukatarsa.