Yan Sanda a Zamfara sun Kama Wata Mata Mai Kaiwa yan Bindiga Makamai

Date:

Jami’an tsaron ‘yan sanda da Hadin gwiwar Wasu kawarrarun Jami’an tsaro a jihar Zamfara sun kama Wata Mai Suna Fatima Lauwali bisa zargin tana safarar Makamai ga Yan Bindiga a Jihar.

Ana zarginta da bayar da makamai da alburusai ga ‘yan bindiga a jihohin Zamfara, Sokoto, Kebbi, Kaduna, Katsina, da Neja.

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, Ayuba Elkana, wanda ya yi holin wadda ake zargin a Gusau a ranar Juma’a, ya ce an kama Fatima mai shekaru 30 a unguwar Gada Biyu da ke karamar hukumar Bungudu, dauke da harsashi guda 991 na AK47 a hannunta, inda ta ce ta na jigilar su ne daga Dabagi Wani Kauye a jihar Sokoto ga wani da ake zargin Dan Bindiga ne mai suna Ado Alero.

A cewar kwamishinan, ta tabbatar da aikata laifin.

CP Elkana, da Tactical Operatives, da kuma hukumar FBI daga hedikwatar rundunar, karkashin jagorancin DSP Hussaini Gimba, sun kuma kama wani Babuga Abubakar bisa zarginsa da laifin taimakawa shugaban ‘yan bindiga, Lawali Na’eka, a karamar hukumar Maradun.

A Gusau, Babuga, Lawali, da Almeriya sun yi awon gaba da shanu 240, a cewar jagoran ‘yan sandan.

Sauran wadanda ake zargin kuma an kama ne bisa yunkurin fyade ga wata karamar yarinya, yunƙurin kisan kai, fashi, da kuma taimakawa ‘yan fashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...