Hukumar tace finafinai za ta fara kamen yan adaidaita sahu a Kano

Date:

Shugaban Hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jahar Kano Alh. Abba El-mustapha ya aike da jami’an Hukumarsa kan manyan titinan Jahar Kano domin sa ido ga matuka baburan adai-daita sahu tare da kama duk wani baburin na adai-daita sahu da aka samu sanye da hotunan batsa ko rubuta kalaman da ba su yi daidai da tarbiya ba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya sanyawa hannu kuma aka aikowa Kadaura24.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Abba El-mustapha ya ce wannan na daga cikin aiyukan da ya rataya a wuyan Hukumar na tabbatar da anyi hoto mai tsafta tare da lika shi a inda ya dace, sannan kuma aikin hukumar ne ta tantance duk wani rubutu kafin ya isa ga idanun a’lummar Jahar Kano.

Yanzu-yanzu: Ganduje ya magantu kan batun komawar Kwankwaso APC

A ya yin da yake gudanar da aikin, Daraktan Dab’i na Hukumar Alh. Abubakar Zakari Garun Babba ya bayyana dangane da yadda ya ga wasu daga cikin matuka baburan adai-daita sahu ke lika hotunan da basu dace ba tare da rubuce rubuce marasa ma’ana wanda yace Hukumar bizata cigaba da lamintar yin hakan ba a fadin Jahar Kano.

InShot 20250309 102403344

A karshen ya yi kira ga matuka baburan na adai-daita sahu da su guji aikata duk wani laifi da zai jamisu fushin Hukumar. Abubakar Zakari ya kuma kara yin kira garesu ta sauran al’umma da su bawa Hukumar hadin Kai tare da goyan baya domin cigaban Jahar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...