Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace bata goyon bayan Hukuncin da kotun ECOWAS ta yanke akan batanci ga Janibin Annabi muhammadu SAW.

A wata sanarwa da Kungiyar ta fitar Mai dauke dasa hannun Babban Sakatare Shehu Tasiu Ishaq da sakataren yada labarai Abubakar Balarabe Kofar Naisa Kungiyar tayi tir da Allah wadai da Hukuncin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kungiyar tace yin Hukuncin ya sabawa dokokin addinin musulunci, Wanda kuma duk wani Hukuncin da zaici Karo da dokokin Ubangiji bazasu goyi bayansa ba.

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Daga nan kungiyar Samarin Tijjaniyya ta kasa tayi kira ga Gwamnati a kowane mataki da lallai a tabbatar dabin dokokin da suka tabbatar da tsarin addinin musulunci akan duk Wanda ya keta alfarmar fiyayyen halitta kamar yadda yake a kundin dokokin shari’ar Musulunci.

Kungiyar kuma ta yabawa Gwamnatin Jihar Kano bisa yadda ta jaddada matsayinta na tabbatar da dokokin da suka shafi hukunta duk Wanda yayi batanci ga Janibin Annabi muhammadu SAW Wanda daman tuni dokokin sun kasance na Gwamnatin Jihar ne.

InShot 20250309 102403344

A don hakane ma Kungiyar ta sake jaddada bukatar mabiya dariqar Tijjaniyya da sauran al’umar Musulmi su cigaba da kasancewa masu son zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma bin dokokin addinin musulunci.

Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta kasa ta sake bukatar Musulmi su dunga kasancewa masu yin ladabi da biyayya tareda kare duk wata Martaba ta Janibin Annabi muhammadu SAW a kalamansu na yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...