Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Date:

Daga Aminu Gama

 

Kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a fagge yan alluna a jihar Kano ta aike wani magidanci da ake zargi da ikirarin bin mamata bashi zuwa gidan gyaran hali.

Mai shari’ar Umar lawan Abubakar na kotu mai lamba 1 a unguwar fagge yan Alluna ne ya bayar da umarnin garkame mutumin har zuwa ranar 14 ga watan 04 2025 domin cigaba da sauraren karar.

Tun da farko lauyan Gwamnati Zaharaddini Mustapha ne ya karantawa wanda ake kara tuhumar da ake yi masa.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ana dai tuhumar mutumin ne da zargin zuwa gidajen da aka yi mutuwa inda yake karyar cewa yana bin wanda ta rasu kudi.

An dai kama mutumin ne yayin da ya je gidan su wani mamacin mai suna Yusuf Mansur Ashura inda ya yi da’awar yana bin mamacin kudi Naira dubu dari uku sakamakon kasuwancin Doya da suka yi.

Sai dai da aka zurfafa bincike sai aka gano mutumin karya yake yi, saboda an sami akalla mutane uku a gidan mutuwar da suka ce sun gane shi, domin mutumin ya taba zuwa ya ce yana bin mamatansu kudade.

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga nan ne aka mika shi ofishinsa yansanda inda su kuma suna kawo shi kotu don ya girbi abun da ya shuka.

Tuni dai wanda ake kara ya amsa laifinsa kuma ya roki mai shari’ar da yayi masa sassauci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...