Buhari ya aiyana Ranar da za’a gudanar da Babban taron APC na Kasa

Date:

Daga Junaidu Saani

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince a gudanar da babban taron jam’iyyar APC na Kasa a watan Fabrairun Shekara ta 2022.
 Shugaban kungiyar gwamnonin APC, Atiku Bagudu ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa a bayan wata ganawar sirri da suka yi da shugaba Buhari a fadar shugaban kasa ta Villa, Abuja a ranar Litinin.
 Taron ya kuma samu halartar shugaban kwamitin riko na jam’iyyar APC Mai Mala Buni wanda kuma shine gwamnan jihar Yobe da kuma gwamna Badaru Abubakar na Jigawa.
 Atiku Bagudu, wanda bai bayyana takamaiman ranar da za a gudanar da babban taron a watan Fabrairu ba, ya ce an sauya Ranar taron ne saboda har yanzu jihohi hudu ba su kammala taronsu ba.
 Ya ce: “A jiya, 21 ga watan Nuwamba, kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, inda muka yiwa kwamitin rikon godiya bisa kokarin da suka yi wajen jagorantar jam’iyyar.  Mun kuma gode wa shugaban kasa da ya ba su goyon baya don cimma aikin da aka dora musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...