Rigakafin Kyanda: An Shirya taron wayar Kan Masu Ruwa da tsaki a K/H Garun Mallam

Date:

Daga Safyan Dantala Jobawa

 

Sashin lafiya na karamar hukumar Garun mallam ya nemi hadin kan iyayen yara don samun nasarar aikin allurar rikafin cutar kyanda.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban sashin Alh Mustapha Ahmad Gambo ya bukacin hakan a wani taro na musamman wanda aka shirya tare da masu ruwa da tsaki na karamar hukumar Wanda aka gudanar a fadar Ajiyan Rano hakimin Garun mallam.
Ya ce sun bukaci hadin kan ne domin samun nasarar aiki wanda za a fara a ranar asabar 20/11/2021 wanda aikin allurar rikafin zai dauki kwanaki 6 ana aiwatarwa.

 Mustapha Ahmad Gambo ya ce allurar rigakafin kyandar za ayi wa yara ‘yan watanni t 9 zuwa shekaru biyar 5 a ka’idance. Sannan ya bayyan wuraren da za a gudanar da aikin allurar a dukkannin asibitocin da ke yankin.

A karshe ya nemi sauran al’umma da su bada hadin kai kamar yadda ya kamata don samun yara Masu  cikakkiyar lafiya yankin dama kasa baki daya.

 A nasu jawaban daban-daban limaman yankin sun sha alwashi bada hadin kai tare da yin kira a cikin hudubobinsu don a Sami nasarar Shirin, haka zalika, sauran dagatai suma sun sh alwashin isar da sakon wayar da kai ga al’ummar su don samun wannan nasarar ta aikin allurar rigakafin cutar kyanda.

A karshe Ajiyan Rano kuma hakimin Garun mallam Alh Lawan Abubakar Madaki ya godewa Sashin lafiya na karamar hukumar bisa irin namijin kokarin da su ke bai wa yankin ba dare ba rana.
 Mahalarta taron sun hada da daukacin Dagatai da manyan Limamai da saura masu ruwa da tsakin yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...