Jam’iyyar PDP Ta Yiwa Ganduje Wankin Babban Bargo

Date:

Shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Osun, Mista Sunday Bisi, ya gargadi Shugaban APC na kasa, Dakta Abdullahi Ganduje, da ya guji yin furucin da zai iya tayar da tarzomar siyasa a yankin Kudu maso Yamma.

Daily Trust ta rawaito cewa Bisi, a cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin, yana mayar da martani ga kalaman da Ganduje ya yi a wajen taro a Jihar Ondo, inda aka rawaito ya ce jam’iyyarsa na da dabarar “mamaye” dukkanin yankin Kudu maso Yamma.

Talla

Shugaban PDP ya gargadi Ganduje cewa irin wadannan kalaman na iya tayar da hankulan jama’a da haifar da rashin zaman lafiya a kasar.

Ya kuma jaddada cewa mutanen Osun za su yanke hukunci kan wanda zai mulke su idan lokacin ya yi.

Gaskiyar abun da ya faru ga yan jaridar gidan gwamnatin Kano har aka sallami wasun su

Yayin da yake bayyana kalaman Ganduje a matsayin “kokari na jefa yankin Kudu maso Yamma cikin rikicin siyasa da ba ya da amfani,” Bisi ya gargadi cewa Najeriya, da tuni take fama da rikice-rikicen kabilanci da kalubalen tattalin arziki, bai kamata a kara tayar mata da hankali ba.

Bisi ya ce, “Ga mutum wanda bai iya cin zabe a jiharsa ta Kano ba, saboda rashin iya mulki a wa’adinsa a matsayin gwamna, ya zo yanzu yana barazanar zuga yankin Kudu maso Yamma da wuta da hayaki ba kawai rashin hankali ba ne, amma rashin tunani ne kwata-kwata.

Talla

“Yayin da Shugaban Kasa ke ci gaba da fuskantar matsalar tattalin arzikin kasar, Ganduje ya kamata ya yi taka-tsan-tsan kada ya kara dagula lamarin ta hanyar kokarin yin magudi a zaben, musamman a yankin Kudu maso Yamma. Yin hakan zai zama tamkar taka kan maciji mai hadari.

Talla

“Idan Mallam Ganduje ya kasa, kamar yadda ya yi, wajen tayar da rikici a Kano, inda aka yi watsi da APC saboda mulkinsa mai tsanani, ya kamata ya shirya karbar irin wannan sakamakon a wasu jihohin da APC ta kasa gamsar da masu zabe.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...