Gwamnatin Kano ta ba da tallafin Naira Miliyan 100 ga wadanda gobarar tankar mai ta shafa a Jigawa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin jihar Kano ta bayar da gudunmawar Naira Miliyan Dari don tallafawa wadanda Iftila’in gobarar tankar mai ta shafa a garin Majiya da ke karamar hukumar Taura a jihar Jigawa.

Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya sanar da bayar da tallafin a yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai wa Gwamna Umar Namadi Danmodi a gidan gwamnati da ke Dutse ranar Alhamis.

Talla

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24, gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada cewa an bayar da tallafin ne domin a kai dauki ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma tallafa wa wadanda suka jikkata yayin gobarar.

Gwamnan ya kuma jajantawa iyalan wadanda suka rasu da kuma wadanda suka samu raunuka, inda ya yi addu’ar Allah ya kiyaye afkuwar irin wannan hali a nan gaba.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya bayyana matukar godiya a madadin al’ummar jihar Jigawa, inda ya godewa jihar Kano bisa irin gudunmawar da ta bayar a wannan mawuyacin lokaci.

Talla

Ya ba da tabbacin cewa za a yi amfani da kudaden cikin adalci wajen taimakon wadanda Iftila’in ya shafa da iyalansu.

Talla

Gwamna Namadi ya kuma bayyana cewa, ya zuwa yammacin ranar Alhamis mutane 167 ne suka rasa rayukansu, kuma mutane 67 ke karbar magani a asibitoci daban-daban a ciki da wajen jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...