Yanzu-yanzu: NNPP ta dakatar da Sakataren gwamnatin Kano da wani kwamishinan

Date:

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin jihar Kano, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da kwamishinan sufuri, Muhammad Diggol daga jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Hashimu Sulaiman Dungurawa ne ya sanar da hakan a yammacin ranar Litinin.

Talla

A cewar Dungurawa, dakatarwar ta biyo bayan korafe-korafensu da ake kaiwa shugabannin mazabunisu da na kananan hukumomi na jam’iyyar.

Dungurawa ya ce an dakatar da su ne saboda rashin mutunta jam’iyyar da shugabancinta.

Tinubu ya buƙaci CAF ta ɗauki mataki kan Libya

“Jam’iyyar ba za ta lamunci duk wani abu na raina shugabancinta da tsarinta ba. Bayan da muka samu wasikun korafe-korafe daga al’umma, sannan kuma muka tabbatar da zargin ta hannun shugabannin kananan hukumomin su, ba mu da wani zabi illa daukar wannan muhimmin mataki,” in ji Dungurawa.

Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ta Arewa a karkashin jagorancin Sulaiman Dambatta, ya kara tabbatar da wannan zargi, wanda ya kai ga yanke hukuncin dakatar da jami’an guda biyu.

Talla

Idan za a iya tunawa a yan Kwanakin nan ana ta zargin Sakataren gwamnatin Kano Dr. Baffa Bichi bisa daukar nauyin wata kungiya mai suna ” Abba tsaya da kararka” wacce take rajin ganin an sami farraku tsakanin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa Rabi’u Musa Kwankwaso.

Solacebase

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...