Yanzu-yanzu: NNPP ta dakatar da Sakataren gwamnatin Kano da wani kwamishinan

Date:

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin jihar Kano, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da kwamishinan sufuri, Muhammad Diggol daga jam’iyyar.

Shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Hashimu Sulaiman Dungurawa ne ya sanar da hakan a yammacin ranar Litinin.

Talla

A cewar Dungurawa, dakatarwar ta biyo bayan korafe-korafensu da ake kaiwa shugabannin mazabunisu da na kananan hukumomi na jam’iyyar.

Dungurawa ya ce an dakatar da su ne saboda rashin mutunta jam’iyyar da shugabancinta.

Tinubu ya buƙaci CAF ta ɗauki mataki kan Libya

“Jam’iyyar ba za ta lamunci duk wani abu na raina shugabancinta da tsarinta ba. Bayan da muka samu wasikun korafe-korafe daga al’umma, sannan kuma muka tabbatar da zargin ta hannun shugabannin kananan hukumomin su, ba mu da wani zabi illa daukar wannan muhimmin mataki,” in ji Dungurawa.

Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ta Arewa a karkashin jagorancin Sulaiman Dambatta, ya kara tabbatar da wannan zargi, wanda ya kai ga yanke hukuncin dakatar da jami’an guda biyu.

Talla

Idan za a iya tunawa a yan Kwanakin nan ana ta zargin Sakataren gwamnatin Kano Dr. Baffa Bichi bisa daukar nauyin wata kungiya mai suna ” Abba tsaya da kararka” wacce take rajin ganin an sami farraku tsakanin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa Rabi’u Musa Kwankwaso.

Solacebase

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...