Majalisar na neman sa kafar wando guda da shugaban ƙasa Tinubu

Date:

Daga  Isa Ahmad Getso

Majalisar wakilan Najeriya ta sa kafa ta rushe lambar girman da shugaban kasa Bola Tinubu ya bai wa shugaban ta Tajudeen Abbas na CFR.

Talla

‘Yan majalisar suka bayyana fusatarsu da ba shi lambar wanda suka bayyana ta a matsayin bata dace da girman kujerarsa ba, inda suka bukaci sauya masa da irin wadda aka bai wa shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ta GCON da kuma babban mai shari’a ta kasa.

Da dumi-dumi: Tinubu zai tafi hutu Burtaniya

Majalisar ta ce babu ban-banci tsakanin Akpabio da Abbas, saboda haka ya dace a bai wa shugaban su irin lambar da aka bai wa Akpabio ta GCON maimakon CFR.

Talla

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito shugaban ƙasa Bola Tinubu ya baiwa wasu mutane lambobin girmamawa na kasa, inda ya baiwa shugaban majalisar wakilai lambar yabo ta CFR, a jawabin da ya yiwa yan Nigeria a ranar cikar kasar Shekaru 64 da samun yancin kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...