Kano: Ganduje Ya Bada Tallafin Naira Miliyan 20 Ga Iyalan Yan Sandan da suka rasu

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Dr. Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya jajantawa iyalan jami’an ‘yan sanda biyar da suka mutu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su yayin da suke dawowa Kano daga jihar Edo.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a makon da ya gabata ne yan Sandan suka yi tsarin yayin da suke hayarsu ta dawowa Kano daga jihar Edo bayan kammala aikin ba da tsaro da suka yi yayin zaɓen gwamnan jihar ta Edo.

Talla

Ganduje ya yi wannan bayyanin ne a babban masallacin Bichi, yayin da yake mika ta’aziyya da addu’o’i ga jami’an ‘yan sandan da suka rasu.

Ya bayyana lamarin a matsayin wani abin bakin ciki ga rundunar ‘yan sanda, da shi kansa, da kuma kasa baki daya.

Tinubu ya nada dan Kano a matsayin shugaban hukumar bunkasa arewa maso yammaci

Jam’iyyar ta bayar da gudummawar Naira miliyan 2 ga iyalan duk jami’an sanya biyar din da suka rasu.

Talla

Sannan ta ba da kyautar Naira miliyan daya ga jami’an yan sanda goma da suka jikkata.

Talla

“Ni da kaina na yanke shawarar zuwa kafa-kafa har Bichi don in mika ta’aziyya ta ga iyalan jami’an ‘yan sandan da suka rasu a bakin aiki.

Shi ma shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar Abubakar Kabir Abubakar, ya mika ta’aziyyarsa, tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...