Nasarar APC a zaɓen Edo ta nuna yan Nigeria sun gamsu da salon mulkina – Tinubu

Date:

Shugaban kasa Tinubu ya taya murna ga dan takarar jam’iyyar APC, a zaben Gwamnan jihar Edo, Sanata Monday Okpebholo bisa nasarar lashe zaben da ya yi.

A juya Lahadi ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, ta sanar da Sanata Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

A sanarwar da mai baiwa shugaban kasa shawara kan fannin yada labarai da dabarun mulki , Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya yabawa shugabannin APC na kasa da na jihar Edo da Gwamnonin jam’iyyar bisa aiki tukuru wajen nasarar ta a zaɓen.

Kwalejin Sa’adatu Rimi: Tsohon kwamishinan ilimi zamanin Kwankwaso ya kalubalanci gwamnatin Kano

Shugaban ya ce, nasarar ta nuna goyan bayan da al’umma ke bai wa manufofin gyaran tattalin arziki, da ma salon mulkin da APC.

Shugaban ya kuma yi kira ga wadanda su ka samu rashin nasara da su yi amfani da hanyoyin shari’a wajen mika kokensu.

Talla

Shugaban ya kuma godewa INEC da jami’an tsaro bisa tabbatar da an yi zaben cikin nasara.

“Ina yabawa hukumar zabe ta INEC da hukumomin tsaro bisa aiki ba dare ba rana wajen gudanar da zaben cikin lumana”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nan gaba kadan za mu bayyana sunayen masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya – Babban Hafsan tsaro

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce...

Wasu yan daba sun ajiye Makamansu a Kano

Gwamnatin Jihar Kano Hadin gwaiwa da Rundunar Yansandan Jihar...

Masu Mukamai a gwamnatin Kano ba su da uzurin kin taimakawa yan Kwankwasiyya – Sanusi Bature

Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin...

Magoya bayan Barr Ibrahim Isa (Matawallen Gwagwarwa) sun aikawa Gwamnan Kano Budaddiyar Wasika

Daga Isa Ahmad Getso Kira don nemawa Barr. Ibrahim Isa...