Zaɓen Edo: Magoya Bayan PDP Sun Fara Zanga-Zanga

Date:

 

Magoya bayan Jam’iyyar PDP, sun fara zanga-zanga yayin da ake dakon sakamakon ƙananan hukumomi biyu da suka rage a Zaɓen Gwamnan Jihar Edo.

Jam’iyyar APC, wadda ita ce babbar jam’iyyar adawa a Edo, tana kan gaba a zaɓen bisa sakamakon da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana.

Hanya ɗaya tak da za a inganta rayuwar yaran da ke barace-barace a Kano da Arewa – Daga Mustapha Hodi Adamu

Magoya bayan PDP, sun mamaye hedikwatar INEC da ke birnin Benin, don yin zanga-zanga kan sakamakon zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar, wanda har yanzu ake ci gaba da ƙirga ƙuri’u.

INEC, ta dakatar da bayyana sakamakon bayan ta bayyana sakamakon ƙananan hukumomi 16 daga cikin 18 da ke jihar.

A halin yanzu, APC ta yi nasara a ƙananan hukumomi 10, yayin da PDP ta yi nasara a ƙananan hukumomi guda shida.

Talla

Ana sa ran INEC za ta sanar da sakamakon sauran ƙananan hukumomi biyu da suka rage a yammacin ranar Lahadi.

Tun da farko daily trust, ta ruwaito yadda APC ta kasance a kan gaba da ƙuri’u 244,549, sai PDP da ƙuri’u 195,954, yayin da jam’iyyar LP ke da ƙuri’u 13,348.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar cigaban Ilimi da gyaran tarbiya ta unguwar zango ta shirya taron kan tarbiyya da tsaro

Daga Rahama Umar Kwaru   Wani Malami a jami'ar Bayero dake...

Gwamnatin Kano ta sanar da Ranar Fara hutun zangon Karatu na 3 ga ɗaliban jihar

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da...

Gwamnatin Kano za ta fara jiyo ra’ayoyin al’umma kafin gudanar da duk wani aiki a jihar – Bilkisu Indabo

Daga Samira Hassan   Gwamnatin jihar Kano ta sha alwashin nan...

Kwankwaso ya gana da Tinubu a fadar shugaban kasa

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso,...