Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta dage ranar komawa da makarantu

Date:

Daga Mubina Mahmoud

 

Gwamnatin jihar Kano ta dage ranar da za a koma makarantun firamare da na sakandire domin fara karatun shekarar 2024/2025.

Wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu ta ruwaito kwamishinan ilimi Alhaji Umar Haruna Doguwa yana bayyana cewa an yanke shawarar dage ranar da za a koma makarantar ne saboda wasu dalilai na gaba gaggawa.

Umar Doguwa ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba ma’aikatar ilimi ta jihar kano za ta sanar da wata rana da za a komawa makarantun.

Farashin man fetur: NNPC ta baiwa Matatar Ɗangote dama

“Ina so in sanar da dalibai da iyayensu cewa sanarwar da aka bayar tun farko na komawa makarantu a ranakun 8 da 9 ga Satumba, 2024, yanzu an dage ta, saboda wasu dalilai na gaggawa da za su taimaka wajen inganta yanayin koyo da koyar da yaranmu. za a sanar da wata ranar nan gaba kadan, “in ji kwamishinan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...