Kungiyar Samarin Tijjaniyya sun Allah wadai da kara kudin man fetur a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta Kasa tayi Allah wadai tare da nuna rahin Jin dadinta bisa tashin gwauron zabi da man fetur yayi a fadin Kasar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kungiyar ta fitar sakamakon sanarwar data fito na Kara farashin mai da kamfanin Samar da man fetur na Kasa yayi.

Sanarwar da Sakataren Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta Kasa Shehu Tasiu Ishaq da sakataren yada labarai na Kungiyar Abubakar Balarabe Kofar Naisa suka sanyawa hannu tace bisa la’akari da halin da “Yan kasa ke ciki akwai bukatar a duba lamarin.

Karin kudin mai: Kayan masarufi kan iya tashi – kungiyar masu masana’antu

Kungiyar ta bukaci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya rage farashin Man fetur din a maimakon Kara farashin sa, domin saukakawa al’umar Najeriya.

Sanarwar daga nan sai ta bukaci al’umar Najeriya su cigaba dayin addu’oi na neman samun sassaucin al’amura da samun cikakken tsaro da wadatar arziki a Kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...