Kungiyar Samarin Tijjaniyya sun Allah wadai da kara kudin man fetur a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta Kasa tayi Allah wadai tare da nuna rahin Jin dadinta bisa tashin gwauron zabi da man fetur yayi a fadin Kasar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kungiyar ta fitar sakamakon sanarwar data fito na Kara farashin mai da kamfanin Samar da man fetur na Kasa yayi.

Sanarwar da Sakataren Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta Kasa Shehu Tasiu Ishaq da sakataren yada labarai na Kungiyar Abubakar Balarabe Kofar Naisa suka sanyawa hannu tace bisa la’akari da halin da “Yan kasa ke ciki akwai bukatar a duba lamarin.

Karin kudin mai: Kayan masarufi kan iya tashi – kungiyar masu masana’antu

Kungiyar ta bukaci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya rage farashin Man fetur din a maimakon Kara farashin sa, domin saukakawa al’umar Najeriya.

Sanarwar daga nan sai ta bukaci al’umar Najeriya su cigaba dayin addu’oi na neman samun sassaucin al’amura da samun cikakken tsaro da wadatar arziki a Kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...