Da dumi-dumi: Sarkin Karaye ya yi sabbin nade-nade

Date:

Daga Umar Ibrahim Kyarana

 

Mai Martaba Sarkin Karaye Alhaji Muhammad Maharaz ya Amince da na din, wasu daga cikin yan majalisar masautar domin cigaba masarautar Karayen.

Wannan shi ne karon farko da sarkin ya yi nade-nade tun bayan da gwamnan jihar kano ya amince da nadin sarkin a matsayin sarki mai daraja ta biyu.

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam’iyyar APCn Kano

Sarkin ya amince da nadin Alh. Balarabe Surajo Karaye a matsayin Wamban Karaye kuma Babban Dan Majalisar Sarki Senior Councillor a Masarautar Karaye, sai Alh Ibrahim Muhammad Karaye a Matsayin Chiroman kuma Shugaban Ma’aikatan Masarautar Karaye, sai Malam Muktar Ishak Idiris a Matsayin Sakataren Masarautar Karaye.

Babban Hadimin Gwamnan Kano ya ajiye Mukaminsa tare da Komawa APC

Jama’ar Masarautar Karaye sun yi murna da wannan Matsayi da Allah ya Baiwa wadannan mutane masu kwazo da kokarin kawo cigaba a yankin Masarautarsa Karaye .

Al’ummar masarautar sun kuma yabawa mai martaba Sarkin Karaye Alh. Muhammad Maharaz bisa kokarin sa na Rungumar kowa domin samar da cigaba a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...