Yanzu-Yanzu: Ganduje ya Sanyawa dokar Kasuwar Kantin kwari hannu tare da Wasu dokokin

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa

 

Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Sanya hannu a dokoki guda 3 Waɗanda Majalisar dokokin Jihar Kano ta zartar da su.

Gwamnan ya Sanya hannu ne yayin taron Majalisar Zartarwar wannna makon, Wanda ya gudana Gidan Gwamnatin Kano.

Jim kadan bayan kammala Sanya Hannu akan Dokokin Wanda Suka kunshi dokar Kasuwar Kantin kwari da kuma ta dokar C P C da aka yiwa kwaskwarima sai Kuma dokar ta Hukumar kula da yawon bude idanu da itama akai Ma ta kwaskwarima.

Dangane da sabuwar dokar Kasuwar Kantin kwari Gwamnan Abdullahi Umar Ganduje ya ce anyi dokar ne Saboda a Kara gyautata al’amuran Kasuwar da Kuma yadda Gwamnati zata Rika Samun kudaden haraji a Kasuwar.

Yace ya Zama wajibi Gwamnati yi dokar Saboda yadda ta Kashe makudan kudade wajen gyaran Kasuwar da Kuma yadda Wasu Yan Kasuwar suke so su Rika bijirewa Gwamnati.

“Wasu Ƙungiyoyi a Kasuwar Suna ganin sun yi karfin da Gwamnati ba zata iya juya su ba, to Amma da Wannan dokar Insha Allah komai Zai tafi yadda ake bukata”. Inji Ganduje

Game da Sauran dokokin kuwa Gwamna Ganduje yace an yi musu gyarane Saboda akwai bukatar hakan don gyautata aiyukan Hukumominsu biyu.

” Dokar CPC zata Kara baiwa al’umma damar su Shigo su bada Gudunmawar su a duk Wani Aikin cigaba da Gwamnati zata gudanar, summan a bangare Ilimi lafiya da dai Sauransu”. Inji Gwamnan

Taron Majalisar Zartarwar na wannna makon ya samu halartar dukkanin ya’yan Majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...