An Kama Malamin Islamiyyar da ya sace dan uwansa a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta ce ta kama wani malamin makarantar Islamiyya bisa zargin sace dan dan uwansa domin karbar kudin fansa.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba ta hannun kakakinta, SP Gambo Isah, rundunar ta ce ta kama malamin mai suna Jamilu Idris da ke karamar hukumar Faskari bisa zargin sace dan dan uwansa, Umar Farouk Kabir, dan shekara hudu.

A cewarta, ranar 9 ga watan jiya Jamilu ya je gidan dan uwansa, Kabiru Abdullahi a Funtua ya sace dansa zuwa garin Dutsen-Alhaji da ke Abuja, babban birnin kasar.

BBC Hausa ta rawaito Rundunar ta ce daga nan ne Jamilu ya kira yayan nasa ya bukaci ya bayar da kudin fansa da suka kai naira miliyan biyar.

Ta kara da cewa mutumin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...