An Kama Malamin Islamiyyar da ya sace dan uwansa a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta ce ta kama wani malamin makarantar Islamiyya bisa zargin sace dan dan uwansa domin karbar kudin fansa.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba ta hannun kakakinta, SP Gambo Isah, rundunar ta ce ta kama malamin mai suna Jamilu Idris da ke karamar hukumar Faskari bisa zargin sace dan dan uwansa, Umar Farouk Kabir, dan shekara hudu.

A cewarta, ranar 9 ga watan jiya Jamilu ya je gidan dan uwansa, Kabiru Abdullahi a Funtua ya sace dansa zuwa garin Dutsen-Alhaji da ke Abuja, babban birnin kasar.

BBC Hausa ta rawaito Rundunar ta ce daga nan ne Jamilu ya kira yayan nasa ya bukaci ya bayar da kudin fansa da suka kai naira miliyan biyar.

Ta kara da cewa mutumin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...