Yan Sanda sun kama ma’auratan da suka sayi jariri, yayin bikin rada masa suna

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta ceto wani jariri dan watanni biyu daga hannun wasu ma’aurata, Mista James da Uwam, a yayin bikin radin sunan yaron a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin,ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya ce ma’auratan sun biya Naira miliyan 2,350,000 don siyan jaririn daga hannun wani da ake zargin mai fataucin yara mai suna Loretta Nelson, wanda ya sayi jaririn a hannun wani Fasto mai suna Peter Udoh a kan N1. 450,000.

Talla
Talla

Hundeyin ya ce Udoh ya sayi jaririn ne a kan Naira 500,000 daga hannun wata mai suna Gloria Sunday da ake zargi da satar jaririn a ranar 11 ga watan Yulin 2024, lamarin da ya sa mahaifiyar jaririn ta kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda.

Zanga-zanga: Tinubu ya ba da umarnin tsaurara tsaro a kan iyakokin Nigeria

Bayan rahoton, Hundeyin ya ce ‘yan sandan sun yi bincike, wanda ya kai su ga cafke wasu da ake zargi da aikata laifin da jami’an ‘yan sanda da ke sashin Oko Oba suka kama.

Ya ce, Jami’an ‘yan sanda sun dauki matakin kama Gloria Sunday wadda a lokacin da ake yi mata tambayoyi ta ce ta sayar da jaririn a kan N500,000 ga wani Fasto Peter Udoh.

Talla

Fasto Udoh, wanda daga baya aka kama shi a garin Ikene, jihar Ogun, ya amince ya sayar da jaririn kan kudi N1,450,000 ga wata Loretta Nelson da aka kama a Festac Town, Legas.

Hundeyin ya ce, Nelson ya amsa cewa ya sayar da jaririn ne a kan Naira 2,350,000 ga wani Mista da Mrs. James Uwam da aka kama yayin bikin nadin yaron da aka sace.

DCL Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Karyata Rahoton Cibiyar Wale Soyinka Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton da...

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Cire Maryam Sanda Daga Jerin Wadanda Za a Yi Wa Afuwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bada umarnin a...

Majalisar Kano ta buƙaci a soke ɗaukar aikin kwastam da aka yi a kwanan nan

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga dukkan...

‎ ‎Kuskure ne Tinubu ya cigaba da ciyo wa Nigeria bashi bayan ya cire tallafin mai – Sarki Sanusi

‎ ‎ ‎Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN),...