Kungiyar Gwamnonin APC Ta Fadi Matsayarka Kan Zanga-zangar Tsadar Rayuwa a Nigeria

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC mai mulki a Nigeria sun ce basu san dalilin da yasa ake shirin, gudanar da zanga-zanga ba a kasar.

Shugaban kungiyar gwamnonin wanda kuma shi gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ne ya bayyana haka lokacin da yake jawabi bayan wani taron nkungiyar gwamnoni Progressives’ Governors Forum (PGF) da aka gudanar a Abuja,in da yace ba mu san masu shirya zanga-zangar me suke shirin yi ba, muna kira da su zo muzauna a tattauna domin samun mafita.

Talla
Talla

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta ruwaito cewa wasu mutane na yin gangamin shirya zanga-zangar da za a yi a fadin kasar daga ranar 1 ga Agusta zuwa 10 ga Agusta, 2024.

Sauyin Yanayi: Za mu fara daukar tsauraran matakai akan masu sare itatuwa barkatai -Gwamnan Kano

“Mu a matsayinmu mun himmatu wajen tabbatar da hadin kan kasar nan, mun himmatu ga duk wani abu da zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, ya kawo wadata, samar da ayyukan yi ga matasa maza da mata wadanda suka kammala karatunsu domin a samar musu aiki yi”. A cewar Uzodimma

Gwamnan Uzodimma ya ci gaba da cewa bai dace a halin yanzu kasar nan ta yi wata zanga-zangar da wata kungiya za ta yi ba, inda ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da wannan zanga-zangar.

Ya kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su yi hakuri da gwamnati, yana mai cewa ana ci gaba da kokarin ganin an daidaita matsalar tattalin arzikin da ake fama da ita a kasar.

ya kara da cewa: “Muna ganin ba hikima ba ne a halin yanzu a yi duk wata zanga-zanga”.

Muna amfani da wannan dama don mu shawarci matasan mu maza da mata da su daina bari ana tunzura su har a haddasa rikici ko hargitsi a kasar nan.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...