Kotu Ta Zauna Kan Shari’ar Kwankwaso Da EFCC

Date:

Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arziƙi Ta’annati (EFCC) ta kasa gabatar da takardu a gaban Babbar Kotun Jihar Kano, wanda hakan ya kawo jinkiri a sauraron shari’ar tsakanin hukumar a da jagoran Jami’yyar NNPP na Kasa, Rabiu Musa Kwankwaso da wasu mutum bakwai.

Masu shigar da ƙarar sun haɗa da NNPP, Dokta Ajuji Ahmed, Dipo Olayanku, Ahmed Balewa, Cif Clement Anele, Lady Folshade Aliu, Injiniya Buba Galadima da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Talla
Talla

EFCC ce wadda ake ƙara a wannan shari’ar.

Tsadar Rayuwa: Yadda Wani Malamin Addinin Musulunci Ya Tallafawa Dalibansa

Lauya masu ƙara, Robert Hon, ya ce a shirye suke domin ci gaba da shari’ar.

Ya nuna cewa EFCC na da kwana biyar don shirya wa shari’ar, amma fiye da kwana 30 ta wuce ba tare da sun shirya ba.

Hon, ya bayyana cewa wannan shari’ar ta shafi ‘yancin ɗan adam ne, inda kuma ya roƙi kotu ta yi watsi da buƙatar EFCC na jinkirta shari’ar ba saboda ba su bayar da ƙwaƙƙwaran dalili.

Talla

Lauyan EFCC, Idris Ibrahim Haruna, ya nemi kotun ta ƙara musu lokaci domin su shirya amsarsu.

Alƙalin kotun, Mai shari’a Yusuf Ubale Muhammad, ya ɗage shari’ar zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, 2024, domin ci gaba da sauraron ƙarar.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...