Zanga-zanga: Tinubu Ya Aike Da Muhimmin Sako Ga Matasan Nigeria

Date:

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu, ya roƙi ’yan Najeriya da su dakatar da zanga-zangar da suka shirya yi a watan Agusta.

Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris, ya ce Tinubu yana son masu shirya zanga-zangar su jira martanin gwamnati game da damuwarsu.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Zanga-zangar da ake gangaminta a Intanet, an shirya yinta ne a watan Agusta kuma za a yi ta ne a duk jihohin Najeriya da babban birnin tarayya, Abuja.

Talla
Talla

Ya zuwa yanzu ba a san waɗanda ke shirya zanga-zangar ba.

’Yan Najeriya na ci gaba da kokawa kan tsadar kayan abinci da kayan masarufi saboda matsalolin tattalin arziki sakamakon cire tallafin man fetur da sauye-sauye ga manufofin musayar kuɗaɗen ƙasashen waje da gwamnatin Tinubu ta yi.

Tsadar Rayuwa: Yadda Wani Malamin Addinin Musulunci Ya Tallafawa Dalibansa

Gwamnatin ta hannun hukumar wayar da kan jama’a ta ƙasa (NOA), da rundunar ‘yan sandan Najeriya, da majalisar wakilai, sun yi gargaɗi game da zanga-zangar.

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya (NLC) da Sanata Ali Ndume sun buƙaci shugaban ƙasa da ya magance matsalolin da matasa suka gabatar.

Kakakin fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya yi gargaɗin cewa zanga-zangar na iya rikiɗewa zuwa tashin hankali da kuma yin ɓarna kamar yadda aka yi a zanga-zangar EndSARS a watan Oktoban 2020, lamarin da ya kai ga asarar dukiya mai tarin yawa.

Talla

Ministan ya ce shugaba Tinubu yana aiki tukuru domin ganin ya cika bukatun al’umma, don haka ya ce babu bukatar matasa sai sun gudanar da zanga-zanga.

” Ba wai muna tsoron ayi mana zanga-zanga ba ne, kawai dai bata cika haifar da da mai ido ba, yanzu ku kalli abun da ya faru a kasashen Sudan,Libiya da dai sauransu, dukkanin su a Sanadiyyar zanga-zanga suka tsinci kawunan su a halin da suke ciki”.

Ya ce shugaba Tinubu ya Dukufa don ganin an baiwa matasan Nigeria tallafin karatu don inganta rayuwar su, da kuma ba tun mafi ƙarancin albashi dukkanin su Shugaba Tinubu ya samar da kudaden da za a gudanar da wannan aikin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...