Zaben APC: Musa Iliyasu kwankwaso yayi Zazzafan Martani ga Mal Ibrahim Shekarau

Date:

Daga Nura Abubakar Bichi

Kwamishinan Raya karkara da cigaban al’umma na Jihar Kano Hon. Musa Iliyasu kwankwaso ya bayyana cewa duk yadda Gwamna Abdullahi Ganduje ya dama Haka za’a Sha a Kano.

Musa Iliyasu kwankwaso ya bayyana hakan a taron Masu Ruwa da tsaki da Gwamna Ganduje ya kirawo a nan domin tattaunawa Kan al’amuran da suka Shafi jam’iyyar APC.

Musa Iliyasu yace Yanzu Abdullahi Umar Ganduje ne Gwamnan Kano Kuma ya Zama wajibi kowa ya bi duk wani abun daya fito dashi in dai a Kano ne.

” A Wannan dakin taro Kabiru Gaya yayi abun da yake so Kwankwaso yayi ,shima Malam Ibrahim Shekaraun yayi yadda yake so, to shima Ganduje tunda shi ne Gwamnan Kano dole abi abun da yace.” Inji Musa Kwankwaso

Kadaura24 ta rawaito Cewa a baya dai Musa Iliyasu kwankwaso ya yiwa Malam Ibrahim Shekarau Kwamishina Lokacin Yana Gwamnan Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...