Zaben APC: Musa Iliyasu kwankwaso yayi Zazzafan Martani ga Mal Ibrahim Shekarau

Date:

Daga Nura Abubakar Bichi

Kwamishinan Raya karkara da cigaban al’umma na Jihar Kano Hon. Musa Iliyasu kwankwaso ya bayyana cewa duk yadda Gwamna Abdullahi Ganduje ya dama Haka za’a Sha a Kano.

Musa Iliyasu kwankwaso ya bayyana hakan a taron Masu Ruwa da tsaki da Gwamna Ganduje ya kirawo a nan domin tattaunawa Kan al’amuran da suka Shafi jam’iyyar APC.

Musa Iliyasu yace Yanzu Abdullahi Umar Ganduje ne Gwamnan Kano Kuma ya Zama wajibi kowa ya bi duk wani abun daya fito dashi in dai a Kano ne.

” A Wannan dakin taro Kabiru Gaya yayi abun da yake so Kwankwaso yayi ,shima Malam Ibrahim Shekaraun yayi yadda yake so, to shima Ganduje tunda shi ne Gwamnan Kano dole abi abun da yace.” Inji Musa Kwankwaso

Kadaura24 ta rawaito Cewa a baya dai Musa Iliyasu kwankwaso ya yiwa Malam Ibrahim Shekarau Kwamishina Lokacin Yana Gwamnan Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...