Ku bamu hadin kai mu kawar duk sharar dake Kano – DMD REMASAB ga al’ummar jihar

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Sabon mataimakin shugaban hukumar kwashe shara ta jihar kano Mukhtar Lamin Hassan yace zasu yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da tsafta a jihar kano duba gudunnawar da gwamnati ke baiwa hukumar karkashin jagorancin Haruna Danzago

Mukhtar Lamin ya bayyana hakan ne a yayin da yake ziyartar wasu guraren da ake kwashe shara a kano domin sanya ido kan yadda aikin ke gudana.

Tinubu ya sauke Sha’aban Sharada daga mukamin da Buhari ya bashi, tare da maye gurbinsa da dan Kano

Lamin Hassan yace ” yazama dole mu yabawa shugaban wanann Hukuma Haruna Dan zago duba da tun bayan kasantuwarsa a shugabancin yake bijiro da aikace-aikace tare da bin lungu da sako domin tabbatar da tsaftarsu, Hakika ina yabawa gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabiru yusuf bisa duba can cantata da ya duba ya nadani a wannan matsayi”.

Har yanzu Nijar taki Bude Bodarta da Nigeria

Yace zai yi duk mai yiwuwa ya bada tasa gudunnawar domin sauke nauyin da gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya dora musu na tsaftace jihar kano daga duk wata shara.

Daga karshe yayi kira ga ma’aikatan Hukumar dasu bashi goyan baya domin cigaba da gudanar da ayyukan da zasu kawo cigaba ga Al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...