Bincike ya nuna yadda rashin aikin yi ya karu a Nigeria, Ina Dalili ?

Date:

Adadin marasa aikin yi a Najeriya ya karu zuwa kashi biyar cikin 100 a rubu’i na uku na shekarar 2023, daidai lokacin da ake fama da matsalar tsadar rayuwa bayan da gwamnati ta cire tallafin man fetur.

Shugaba Bola Tinubu ya kare manyan sauye-sauyen da ya yi guda biyu da suka haɗa da cire tallafin man fetur da kuma barin kasuwa da tantance darajar naira, inda ya ce duk da cewa hakan zai haifar da wahalhalu na kankanin lokaci, suna da muhimmanci wajen samar da masu zuba hannun jari da habaka kuɗaɗen gwamnati.

Hukumar Kididdiga ta Kasa NBS ta ce adadin marasa aiki ya tashi daga kashi 4.2 cikin 100 a cikin kwata na baya.

Cikakken Bayanin Yadda Shari’ar Murja Kunya ta Gudana Yau a Kotu

Adadin marasa aikin yi a tsakanin matasa masu shekaru 15-24 ya tashi zuwa kaso 8.6 daga kaso 7.2.

Rashin aikin yi a cikin birane shi ma ya ƙaru kaɗan zuwa kaso 6 daga kaso 5.9 a rubu’in da ya gabata.

Rundunar Sojin sama ta kama ƙasurgumin mai garkuwa da mutane a Kano

Najeriya wadda ita ce ƙasa mafi yawan al’umma a Afirka mai sama da mutane miliyan 200, ta yi fama da marasa aikin yi tsawon shekaru da dama, sakamakon ƙaruwar yawan al’umma da ya zarce ci gaban tattalin arzikin ƙsar.

Adadin ayyukan yi na yau da kullun, wanda ke auna yawan ma’aikata a cikin tattalin arziki ya sami canji kaɗan da kaso 92.3, a cewar NBS, aikin ma’aikata shi ma ya faɗi kaɗan zuwa kaso 79.5 daga kaso 80.4 a cikin kwata na biyu.

BBC Hausa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu y ba da umarnin sake Karya farashin kayan Abinci a Nigeria

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bai wa wani...

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Kulla Alaka Don Inganta Kwarewar Turanci da Samar da Damar Karatu Ga Dalibai A Duniya

  Gamayyar rukunin jami’o’in MAAUN ta kulla yarjejeniyar hadin gwiwar...

Hasashe 6 da Musa Iliyasu Kwankwaso ya yi kuma suka tabbata a siyasar Kano

‎ ‎ ‎ ‎Musa Iliyasu Kwankwaso na daga cikin fitattun ’yan siyasar...

Hukumar Hisbah Za ta Tura Sama da Jami’ai 1,000 Don Samar da Tsaro a Ranar Takutaha a Kano

Hukumar Hisbah ta Karamar Hukumar Birni a Jihar Kano...