Jam’iyyar APC ta Karrama Musa Iliyasu Kwankwaso

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Jam’iyyar APC ta kasa reshen jihar kano ta karrama guda cikin jagororinta Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso saboda gudunnawar da ya baiwa jam’iyyar tun kafin zabe da kuma bayan zaɓen shekara ta 2023 a jihar Kano.

” Kwamitin yakin neman zaben Gawuna da Garo yan takarar gwamnan kano a shekarar 2023, sune suka zauna suka ga ya dace su karrama ka saboda gudunnawar da ka bayar wajen wayar da kan yan jam’iyyar a kafafen yada labarai tun daga farkon takarar su har zuwa karshe”.

Kotun Ƙoli: Shin da gaske ne an kwalla yarjejeniya tsakanin Gwamnan Kano da Tinubu ?

Kadaura24 ta rawaito Darakta Janar na kwamitin yakin neman zaben Gawuna da Garo Alhaji Rabi’u Sulaiman Bichi ne ya Mika lambar yabon ga Musa Iliyasu Kwankwaso domin yaba masa kan aiyukan da ya gudanar.

” Duk Kano babu wanda ya bayar da gudunmuwar da ka bayar a kafafen yada labarai kan takarar Gawuna da Garo, hakan tasa muka ga dacewar mu karramaka don mu kara maka kwarin gwiwar cigaba da tallata manufofin jam’iyyar APC a Kano da Nigeria baki daya “. Inji Bichi

Rabi’u Sulaiman Bichi wanda tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano ne yace akwai bukatar dukkanin jagorori da yan jam’iyyar APC na jihar kano da kasa baki daya suyi koyi da kai ” babu shakka da koya a APC irinka ne da mun sami cigaban da yafi wanda muke ciki a yanzu”.

Malam Shekarau ya yi tsokaci Kan Kiran da Ganduje ya yiwa Gwamnan Kano na Komawa APC

Da yake nasa jawabin Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso ya godewa kwamitin yakin neman zaben Gawuna da Garo bisa karramawar da sukai masa, sannan yace yayi abun da yayi ne domin samun nasarar yan takarar da jam’iyyar APC baki daya.

” Ina baka tabbacin zamu cigaba da kare martaba da mutuncin jam’iyyar APC a jihar Kano, saboda muna da yakinin al’ummar jihar suna kaunar yan takarar mu da jam’iyyar mu, don haka ba za mu saurara ba wajen kare martabar APC”. A cewar Kwankwaso

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito tun kafin zabe Musa Iliyasu Kwankwaso yake tallata manufofin jam’iyyar APC da na yan takarar ta na gwamnan kano, kuma har aka shiga kotu shi kadai ne a cikin jagororinta yake fita kafafen yada labarai don sanar da yan jam’iyyar halin da ake ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...