Sarkin Kano ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama ta Sumaila

Date:

Daga Khadija Abdullahi Umar

An nada Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin uban jami’ar Al-Istiqama dake garin Sumaila a jihar Kano.

Shugaban Jami’ar Hon. Abdulrahman Kawu Sumaila ne ya gabatar da takardar nadin ga Mai Martaba Sarkin Kano a ranar Larabar nan.

Da yake mika takardar ga Mai Martaba sarkin Kawu Sumaila yace sun yi la’akari da kwarewa kogewa da Sarkin yake dasu tare da kokarin da yake yi wajen inganta harkokin Ilimi a jihar Kano da Kasa baki daya.

A Jawabinsa Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nuna farin Cikinsa tare da bada tabbacin Zai yi duk mai yiwuwa wajen cigaban Jami’ar dama Ilimi baki daya.

Mai martaba sarkin ya bukaci mawadata dake cikin al’umma da su mai da hankali wajen bada tasu Gudunmawar don cigaba Ilimi a Kano da Kasa baki daya

23 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...