Sarkin Kano ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama ta Sumaila

Date:

Daga Khadija Abdullahi Umar

An nada Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin uban jami’ar Al-Istiqama dake garin Sumaila a jihar Kano.

Shugaban Jami’ar Hon. Abdulrahman Kawu Sumaila ne ya gabatar da takardar nadin ga Mai Martaba Sarkin Kano a ranar Larabar nan.

Da yake mika takardar ga Mai Martaba sarkin Kawu Sumaila yace sun yi la’akari da kwarewa kogewa da Sarkin yake dasu tare da kokarin da yake yi wajen inganta harkokin Ilimi a jihar Kano da Kasa baki daya.

A Jawabinsa Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nuna farin Cikinsa tare da bada tabbacin Zai yi duk mai yiwuwa wajen cigaban Jami’ar dama Ilimi baki daya.

Mai martaba sarkin ya bukaci mawadata dake cikin al’umma da su mai da hankali wajen bada tasu Gudunmawar don cigaba Ilimi a Kano da Kasa baki daya

23 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...